Kocin Manchester City, Pep Guardiola, ya amince zai gane idan zakarun gasar Premier suka yanke shawarar korar shi sakamakon rashin nasara da ya yi.
City ta samu nasara sau daya ne a wasanni 10 da ta buga bayan ta sha kashi a hannun Juventus da ci 2-0 a ranar Laraba.
Mutanen Guardiola a halin yanzu suna matsayi na 22 a teburin gasar zakarun Turai, maki biyar tsakaninta da wuraren cancantar kai tsaye yayin da wasanni biyu suka rage.
Haka kuma suna mataki na hudu a teburin gasar da tazarar maki takwas tsakaninta da Liverpool wadda itama ke da wasa a hannu.
Guardiola ya samu nasara sosai tun lokacin da ya karbi ragamar City a 2016 kuma bai taba samun irin wannan rawar gani a baya ba.
Tsohon dan wasan Barcelona da Bayern Munich ba a taba korar shi ba a rayuwarsa.
Amma da yake magana da tsohon abokin wasansa na Brescia Luca Toni akan Firimiya Video Sport, Guardiola ya ce: “Shin Man City za ta tura ni gida? Idan haka ne, zan koma gida.
“Me zaki iya yi a rayuwa? Rayuwa ba koyaushe take tafiya yadda mutum yake so ba.”