Kocin Manchester City, Pep Guardiola, ya ce kungiyarsa ba za ta iya lashe gasar cin kofin Premier ba, idan ta sha kashi a hannun Liverpool a karshen mako mai zuwa.
Guardiola na magana ne bayan da zakarun suka yi rashin nasara a wasa na biyar a jere a dukkan gasa da kuma wasan gasar Premier na uku da ci 4-0 a hannun Tottenham a ranar Asabar.
Reds za ta iya samun tazarar maki takwas idan ta doke Southampton a ranar Lahadi.
An tambayi Guardiola ko tazarar maki 11 – idan City ta yi rashin nasara a hannun kungiyar Arne Slot – zai yi yawa don yin garambawul ko da a wannan matakin na kakar wasa.
Ya amsa: “Eh, gaskiya ne.
“Ba mu tunanin yin nasara ko rasa [kambun], ba mu cikin halin da za mu yi tunanin abin da zai faru a karshen kakar wasa ta bana.
“Idan a karshe ba mu yi nasara ba saboda ba mu cancanci hakan ba. Mun samu nasara a baya saboda mun cancanci hakan.”