Ivory Coast ta tarbi sojojinta da aka tsare tsawon wata shida a Mali, lamarin da ya haifar da takun-saƙa tsakanin ƙasashen biyu.
Jami’an tsaron su 46, sun isa wani filin jirgin sama a Abidjan sanye da kakin soji suna murmushi riƙe da tutar ƙasar.
An tura sojojin Najeriya 65 zuwa Mali
Faransa ta kwashe sojojin ta daga Mali baki ɗaya
Sojojin Mali da ke mulki a ƙasar ne suka yi musu afuwa ranar Juma’ar da ta gabata
Dakarun dai sun samu tarba ne daga shugaban ƙasar Alassne Ouattara da wasu manyan jami’ai a ƙasar.