‘Yan gudun hijira da neman mafaka na ci gaba da tururuwar shiga kasar Moldova, abin da ya janyo shugaban kasar ke neman taimakon kasashen duniya kan yadda za ta yi.
“Muna da mutum 270,000 wadanda suka tsallako iyaka,” In ji Firaiministar Maldova Natalia Gavrilița ta shaida wa BBC.
“Sama da mutum 100,000 sun aminta su zauna na wucin gadi. Ga kasa irin Maldova wannan ba karamin adadi ba ne.”
Moldova, karamar kasa ce da ke da yawan mutane miliyan 2.5 tsakanin Ukraine da Romania, daya kuma daga cikin kasashen Turai masu fama da matsalar tattalin arziki.
Yanzu adadin ‘yan Ukraine ya karu da kashi 4 cikin 100 zuwa kasarmu.