fidelitybank

Malaysia na shirin kawo karshen hukuncin kisa

Date:

Gwamnatin Malaysia na shirin soke hukuncin ɗaurin rai da rai da kuma na kisa kan laifuka shida, domin yin garanbawul ga tsarin shari’ar ƙasar.

Dokar da aka gabatar za ta bai wa alkalai ikon yanke hukunci kan yadda za a hukunta waɗanda aka samu da laifuka daban-daban, kama daga safarar miyagun kwayoyi zuwa kisa.

Ministar shari’a da sake fasalin hukumomin Malaysia, Azalina Usman Saeed, ta shaida wa majalisar dattijai a birnin Kuala Lumpur cewa za a gabatar da kudurin doka kan sauye-sauyen da ake shirin gabatarwa a majalisar dokokin ƙasar a ranar 27 ga watan Maris.

Dokokin Malaysia na yanzu sun tanadi hukuncin kisa kan laifuka 34 da suka haɗa da kisan kai da fataucin miyagun kwayoyi da kuma ta’addanci a ƙasar da ke kudu maso gabashin Asiya.

Mai magana da yawun ma’aikatar shari’a da sake fasalin hukumomin Malaysia, ya ce a cikin sabbin shawarwarin, hukuncin kisa ba zai sake shafar laifukan da suka shafi safarar bindigog da kera makamai da kuma yin garkuwa da mutane ba, inda za a yanke musu hukuncin ɗaurin shekaru arba’in a gidan yari ko bulala maimakon kisa.

Hukuncin kisa zai kasance zaɓi ne ga alkalai yayin da ake fuskantar wasu laifuffuka da suka haɗa da ta’addanci da kuma kai hari ga masarautar Malaysia.

naija news legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp