Wani malami da aka yi garkuwa da shi tare da ’yan makarantar Kuriga a karamar hukumar Chikun ta Jihar Kaduna, ya rasu ne a lokacin da ake garkuwa da shi.
Gwamna Uba Sani ya bayyana hakan a cikin shirin Siyasa na Lahadi na gidan Talabijin na Channels.
Gwamnan ya bayyana cewa, sojoji tare da hadin gwiwar kananan hukumomin jihar Zamfara ne suka ceto dukkan yaran makarantar da ‘yan ta’addan suka sace.
Ya yi nadamar yadda malamin ya kasa rayar da shi sakamakon matsalar rashin lafiya yayin da yake hannun wadanda suka sace shi.
Gwamnan ya bayyana cewa, “mutum daya ne bai dawo ba, shi ne malami.
“Gaskiyar lamarin kenan, amma dukkan yaran 137 sun dawo lafiya.”