fidelitybank

Malamin Coci ya gargaɗi Tinubu cewa dala za ta iya kaiwa 1,700 yayin da shinkafa buhu ta kai 90,000

Date:

Shugaban cocin INRI Evangelical Spiritual Church, Primate Elijah Ayodele, a ranar Litinin ya gargadi shugaban kasa Bola Tinubu cewa dala za ta iya kaiwa Naira 1,700, sannan za a sayar da buhun shinkafa kan N90,000.

Ya ce kamata ya yi Tinubu ya daure wa matsalar tattalin arziki da ke tafe matukar ba a samar da mafita don kawo karshen rudanin da kasar nan ke fama da shi ba.

A wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Osho Oluwatosin ya sanya wa hannu, Primate Ayodele ya bayyana cewa idan shugaban kasar bai yi abin da ake bukata ba, tattalin arzikin Najeriya ba zai daidaita ba har zuwa 2026.

Ya shawarci gwamnati da ta samar da tsaro, ta durkusar da farashin kayan masarufi, samar da isasshiyar wutar lantarki da inganta kayayyakin cikin gida domin a yi karo da dala da kuma saukaka wa ‘yan Najeriya nauyi.

Bawan Allah ya bayyana cewa matakan da gwamnatin ta dauka kawo yanzu ba za su taimaki kasar nan ba illa kara hauhawar farashin kayayyaki.

A cewar Ayodele: “Idan gwamnatin Tinubu ba ta yi abin da ake bukata ba, tattalin arzikin ba zai daidaita ba har zuwa 2026.

“Suna bukatar samar da tsaro, rage farashin kayayyakin abinci, samar da isasshiyar wutar lantarki da inganta kayayyakin cikin gida. Wannan zai taimaka wa gwamnati kuma zai lalata dala.

‘’Duk wadannan matakan da suke dauka ba za su yi tasiri ba; kawai zai haifar da hauhawar farashin kayayyaki. Idan ba su yi abin da ya dace ba Najeriya za ta sayi dala kan Naira 1,700, buhun shinkafa zai kai Naira 90,000 kuma zai kashe tattalin arzikin kasa. Da alama ba su da ra’ayoyin ba za su taimaka lamarin ba.”

sunnnewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp