Kimanin malaman makarantu 9,204 ne daga sassan kasar nan a ranar Asabar din da ta gabata ne suka rubuta jarabawar neman cancantar koyarwa (PQE) ga malaman da kungiyar rijistar malamai ta Najeriya (TRCN) ta shirya.
Darakta mai rikon kwarya da bayar da lasisi, Dakta Jacenta Ogboso ta bayyana hakan a lokacin da ake sa ido kan yadda ake gudanar da jarabawar a makarantar SASCON International School, Maitama, Abuja. In ji The Nation.
Ogboso ta ce Majalisar ta sake dage atisayen a Sokoto da Zamfara saboda matsalolin tsaro da aka fuskanta a baya-bayan nan.
Ta kuma bayyana cewa, mutane 125 ne suka yi rajistar wannan atisayen a Sokoto yayin da 151 suka yi rajista a jihar Zamfara, inda ta kara da cewa za a dage jarabawar a jihohin biyu da zarar an samu sauki.
Babban sakataren ma’aikatar ilimi ta tarayya, David Adejo, ya ce malaman da ba su yi rajistar rubuta PQE ba ba malamai ba ne a Najeriya.
Ya ce Gwamnatin Tarayya ta yi niyyar daidaita harkar koyarwa.