fidelitybank

Malaman Da’awah 6 sun mutu a hadarin mota a Kano

Date:

Mummunan hatsarin mota ya lakume rayukan malaman addinin musulunci guda shida a jihar Kano a ranar Laraba bayan gudanar da aikin yada addinin musulunci na Da’awah.

DAILY NIGERIAN ta tattaro cewa, malaman na dawowa ne daga Da’awah da ke karamar hukumar Sumaila, wanda Imam Malik Islamic Foundation ya tallafa musu.

Wasu ma’aikatan gidauniyar da ba su so a ambaci sunanta sun ce sun samu labarin faruwar lamarin da misalin karfe 3:00 na rana.

A cewarta, bayanan da suka samu sun nuna cewa dukkanin malamai shida, wadanda su ne shugabannin Da’awah sun rasu.

Ta kara da cewa babu wani bayani kan makomar sauran ma’aikatan da suka raka malaman addinin musulunci a Sumaila.

Ta ce wadanda suka mutun na karkashin jagorancin Sheikh Alkassim Zakariyya, wanda shi ma ya rasu a hadarin.

legit news 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...

Ƴan sanda sun kama mutum 26 da ake zargi da hannu a kashe-kashen Benue

Sufeto Janar na ‘ƴan sanda, Kayode Egbetokun, ya bayyana...

Ba dan mun yi wa Iran barna ba da har yanzu ba ta nemi sulhu ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake jaddada cewa harin...

Iran ta zartar da hukuncin kisa kan masu leken asiri

Kamfanin dillancin labarai na sashen shari'a a Iran ya...

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...
X whatsapp