Mummunan hatsarin mota ya lakume rayukan malaman addinin musulunci guda shida a jihar Kano a ranar Laraba bayan gudanar da aikin yada addinin musulunci na Da’awah.
DAILY NIGERIAN ta tattaro cewa, malaman na dawowa ne daga Da’awah da ke karamar hukumar Sumaila, wanda Imam Malik Islamic Foundation ya tallafa musu.
Wasu ma’aikatan gidauniyar da ba su so a ambaci sunanta sun ce sun samu labarin faruwar lamarin da misalin karfe 3:00 na rana.
A cewarta, bayanan da suka samu sun nuna cewa dukkanin malamai shida, wadanda su ne shugabannin Da’awah sun rasu.
Ta kara da cewa babu wani bayani kan makomar sauran ma’aikatan da suka raka malaman addinin musulunci a Sumaila.
Ta ce wadanda suka mutun na karkashin jagorancin Sheikh Alkassim Zakariyya, wanda shi ma ya rasu a hadarin.