fidelitybank

Malamai ku yi wa’azin da al’umma za su zauna lafiya – Buni

Date:

Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya bukaci shugabannin gargajiya da na addini da su yi wa’azin zaman lafiya tsakanin al’ummarsu.

Buni ya bayyana hakan ne a ranar Larabar da ta gabata a wani sakon Sallah ta hannun mai magana da yawunsa, Mamman Mohammed a Damaturu.

“Bari in yi kira ga matasanmu da su yi bikin Sallah lafiya, musamman tare da kiyaye dokokin hanya.

“Hukumomin tsaro za su tabbatar da bin doka da oda don gudanar da bukukuwan Sallah cikin lumana da nasara”, in ji Gwamna Buni.

A lokacin da yake taya al’ummar musulmi murnar zagayowar bikin Eid-el-Kabir Sallah, gwamnan ya tabbatar wa al’ummar jihar cewa gwamnatinsa za ta mayar da hankali wajen samar da kayayyakin more rayuwa da inganta rayuwar jama’a.

“A sabon salon za mu inganta dogaro da kai da samar da ayyukan yi don ci gaban tattalin arzikin jama’armu, musamman matasa”, in ji shi.

Ya kuma bada tabbacin bude kofa domin bawa kowa damar shiga da kuma bada gudumawa ga cigaban jihar ba tare da la’akari da bambancin al’adu da siyasa ba.

Buni ya kuma yi addu’ar Allah SWT ya karbi addu’o’i da layya da addu’o’in muminai.

network news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp