fidelitybank

Maku ya janye daga neman takarar gwamna

Date:

Tsohon ministan yada labarai kuma dan takarar gwamna a jam’iyyar PDP, Labaran Maku ya janye aniyarsa na tsayawa takarar gwamna sa’o’i bayan fara kada kuri’a.

Maku ya bayyana haka ne a ranar Laraba a wurin da za a gudanar da zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a karamar hukumar Nasarawa Toto bayan wata ‘yar gajeriyar ganawa da wasu masu ruwa da tsaki na jam’iyyar.

Da yake mayar da martani kan janyewar tasa, Maku ya ce bayan tattaunawa da abokansa da abokan huldarsa ya yanke shawarar janye aniyarsa ta tsayawa takara a zaben fidda gwani.

Da aka tambaye shi ra’ayinsa kan yadda zaben fidda gwanin da ke gudana tsohon ministan ya ce ‘Babu Magana.

Idan dai za a iya tunawa, Daily Sun ta ruwaito cewa dukkan ‘yan takarar guda uku, David Ombugadu, Nuhu Amgbazu da Labaran Maku, sun amince su yi aiki tare domin kayar da wanda ke kan karagar mulki.

sun news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naɗa kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka ƴanbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe ƴanbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...

Wike ya caccaki Rotimi a kan jam’iyyar ADC

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya caccaki tsohon...

Tsige ni daga mukamin Wazirin Gaya ba a kan doka ba ne – Usman Alhaji

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano, Alhaji Usman Alhaji, ya...

Gini mai bene uku ya danne Mutane a jihar Legas

Wani gini mai bene uku ya rufta a unguwar...

Kotu ta daure Matashi dan Tiktok da ya ke sanya rigar mama

Wata kotu a jihar Kano, ta yanke wa wani...

Peter Obi ka gaggauta ficewa daga jam’iyyar mu nan da awa 48 – Labour Party

Bangaren jam’iyyar Labour da Julius Abure ke jagoranta, ya...
X whatsapp