Shugaban kasa Muhammadu Buhari na ganawa da daya daga cikin masu neman takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC mai mulki, Gwamna Yahaya Bello.
Taron dai yana gudana ne a fadar shugaban kasa dake Abuja.
Gwamnan Kogi na cikin mutane 23 da ke neman takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC da aka amince da su a zaben fidda gwani na jam’iyyar.
Duk da cewa Gwamnonin APC daga Arewa sun yanke shawarar cewa mulki ya koma Kudu, Bello ya nesanta kansa da kudurin.
Ba a dai bayyana ganawar da shugaban kasa da gwamnan ya yi ba, amma akwai rade-radin cewa Bello zai iya tattaunawa da shugaban kasa kan matakin da ya dauka kan ko zai sauka ko a’a.