fidelitybank

Makoci ya kashe Makocinsa a kan Shinkafa

Date:

Wani rikici kan rabon shinkafa ya kai ga mutuwar wani matashi mai suna Christian, wanda aka ce maƙwabcinsa Daniel Onyejekwe, mai shekaru 30, ya daba wa wuƙa a garin Sapele, Jihar Delta.

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Delta ta tabbatar da kamen Onyejekwe, wanda ake zargi da aikata kisan kai yayin hatsaniyar da ta ɓarke a lokacin rabon shinkafa a yankin Ogwanja, kan titin Boyo Road.

Mai magana da yawun rundunar, SP Bright Edafe, ya bayyana cewa, “Rikicin ya faru ne a yayin rabon shinkafa inda aka samu musayar yawu da ya rikide zuwa faɗa.

“Daga nan ne Onyejekwe ya yi amfani da kwalɓa ya daba wa Christian, wanda hakan ya kai ga mutuwarsa.”

Ganau sun shaida cewa bayan samun raunuka masu tsanani, wata ƙungiyar vigilante ta garin ta yi ƙoƙarin ceto Christian ta hanyar kai shi asibiti, amma likitoci sun tabbatar da mutuwarsa a lokacin da aka isa.

“Mun fara bincike kan lamarin, kuma muna tabbatar wa da jama’a cewa wanda ake zargi zai fuskanci hukunci daidai da abin da doka ta tanada,” in ji SP Edafe.

A halin yanzu, gawar Christian an ajiye ta a ɗakin ajiye gawa yayin da bincike kan dalilin rikicin da kuma yadda lamarin ya faru ke ci gaba.

legitnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp