fidelitybank

Makoci ya kashe Makocinsa a kan Shinkafa

Date:

Wani rikici kan rabon shinkafa ya kai ga mutuwar wani matashi mai suna Christian, wanda aka ce maƙwabcinsa Daniel Onyejekwe, mai shekaru 30, ya daba wa wuƙa a garin Sapele, Jihar Delta.

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Delta ta tabbatar da kamen Onyejekwe, wanda ake zargi da aikata kisan kai yayin hatsaniyar da ta ɓarke a lokacin rabon shinkafa a yankin Ogwanja, kan titin Boyo Road.

Mai magana da yawun rundunar, SP Bright Edafe, ya bayyana cewa, “Rikicin ya faru ne a yayin rabon shinkafa inda aka samu musayar yawu da ya rikide zuwa faɗa.

“Daga nan ne Onyejekwe ya yi amfani da kwalɓa ya daba wa Christian, wanda hakan ya kai ga mutuwarsa.”

Ganau sun shaida cewa bayan samun raunuka masu tsanani, wata ƙungiyar vigilante ta garin ta yi ƙoƙarin ceto Christian ta hanyar kai shi asibiti, amma likitoci sun tabbatar da mutuwarsa a lokacin da aka isa.

“Mun fara bincike kan lamarin, kuma muna tabbatar wa da jama’a cewa wanda ake zargi zai fuskanci hukunci daidai da abin da doka ta tanada,” in ji SP Edafe.

A halin yanzu, gawar Christian an ajiye ta a ɗakin ajiye gawa yayin da bincike kan dalilin rikicin da kuma yadda lamarin ya faru ke ci gaba.

legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp