fidelitybank

Makiyaya sun kashe Zakunan da suka addabe su

Date:

Makiyaya sun kashe wasu zakuna shida a gundumar Kajiado na ƙasar Kenya, bayan da zakunan suka kwashe tsawon daren Asabar suna far wa mazauna ƙauyen Nashipa.

Rahotonni sun ce zakuna 11 da suka tsere daga gandun dajin ‘Amboseli National park’, suka afka wa ƙauyen tare da addabar al’ummar ƙauyen na tsawon dare guda.

Zakunan sun yi ta far wa gidajen mutane inda suka kashe tumaki 11 tare da kare guda, a wani lamari da wani mazaunin ƙauyen ya bayyana da ‘daren subhana’.

“Yunkurin da masu tumakin suka yi na ƙubutar da su ya ci-tura, tumaki ne da suka tsallake-rijiya-da-baya daga masifar fari da ƙasarmu ke fuskanta, amma sai ga shi sun ƙare a matsayin kalacin zakuna,” in ji wani mazaunin ƙauyen.

A ranar Asabar da safe ne gwamman mazauna ƙauyen suka ɗauke da kwari da baka da wasu makaman suka ƙaddamar da farautar zakunan tare da kashe shida daga cikinsu.

Jami’an kula da gandun dajin ƙasar da jagororin kauyen da sauran masu ruwa da tsaki sun gudanar da ganawar gaggawa kan lamarin da maraicen ranar Asabar.

sani ahmad

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp