fidelitybank

Makiyaya sun kashe Zakunan da suka addabe su

Date:

Makiyaya sun kashe wasu zakuna shida a gundumar Kajiado na ƙasar Kenya, bayan da zakunan suka kwashe tsawon daren Asabar suna far wa mazauna ƙauyen Nashipa.

Rahotonni sun ce zakuna 11 da suka tsere daga gandun dajin ‘Amboseli National park’, suka afka wa ƙauyen tare da addabar al’ummar ƙauyen na tsawon dare guda.

Zakunan sun yi ta far wa gidajen mutane inda suka kashe tumaki 11 tare da kare guda, a wani lamari da wani mazaunin ƙauyen ya bayyana da ‘daren subhana’.

“Yunkurin da masu tumakin suka yi na ƙubutar da su ya ci-tura, tumaki ne da suka tsallake-rijiya-da-baya daga masifar fari da ƙasarmu ke fuskanta, amma sai ga shi sun ƙare a matsayin kalacin zakuna,” in ji wani mazaunin ƙauyen.

A ranar Asabar da safe ne gwamman mazauna ƙauyen suka ɗauke da kwari da baka da wasu makaman suka ƙaddamar da farautar zakunan tare da kashe shida daga cikinsu.

Jami’an kula da gandun dajin ƙasar da jagororin kauyen da sauran masu ruwa da tsaki sun gudanar da ganawar gaggawa kan lamarin da maraicen ranar Asabar.

tribune news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp