fidelitybank

Makiyaya sun kashe mutane uku a Binuwai zuwa Nasarawa

Date:

A kalla mutane uku ne wasu makiyaya dauke da makamai suka kashe tare da jikkata wasu a hanyar Benue zuwa Nasarawa a ranar Juma’a.

Makiyayan dauke da bindigogi sun kai harin kwantan bauna a kan hanyar Makurdi-Lafia mai cike da cunkoson jama’a da ke kusa da Ortese a karamar hukumar Guma ta jihar Binuwai, lamarin da ya yi sanadin mutuwar matafiya uku tare da jikkata wasu da dama.

Wannan lamarin ya faru ne kimanin mako guda bayan da wasu makiyaya dauke da makamai suka yi wa wasu ‘yan gudun hijira uku kwanton bauna, wadanda suka je kamun kifi a karamar hukumar Gwer ta Yamma a jihar Benue.

A cewar wata majiya mai tushe, maharan sun yi kwanton bauna a kan hanyar Makurdi-Lafia mai cunkoson jama’a a yammacin ranar Alhamis da safiyar Juma’a, inda suka auna wa matafiya marasa laifi a kusa da Hirnyam.

Mista Christopher Waku, sakataren tsaro na karamar hukumar Guma, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa maharan sun shafe kwanaki biyu a jere suna kwanton bauna a kusa da Ortese, akan hanyar Daudu/Ortese dake kan babbar hanyar Makurdi zuwa Lafia. A yayin wadannan hare-haren, sun bindige mutane uku tare da kashe dukkansu mazauna yankin.

“Ba wani shingen hanya ba ne; makiyayan dauke da makamai sun tsaya akan titin Daudu Ortese. Sun kashe mutane biyu ne a ranar Alhamis din da ta gabata da misalin karfe 5 na yamma, tare da jikkata wani mutum daya wanda a halin yanzu yake jinya a asibitin koyarwa na jami’ar jihar Benue (BSUTH).

“A yau, da safiyar Juma’a, sun kashe wani mutum, wanda ya kawo adadin wadanda suka mutu zuwa uku. Abin takaici, duk wadanda abin ya shafa mazauna yankin ne,” in ji Waku.

punch news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp