fidelitybank

Makiyaya da Manona sun tayar da zaune tsaye a Kwara

Date:

Rikicin da ya barke tsakanin manoma da Fulani makiyaya a kauyen Rogu da ke karamar hukumar Patigi a jihar Kwara, ya yi sanadin mutuwar mutum guda.

DAILY POST ta tattaro cewa biyo bayan mutuwar manomin, wasu fulani manoma ne suka mamaye sansanin Fulani da ke kauyen.

Mamaya ya biyo bayan rikicin da ya barke tsakanin manoma da Fulani makiyaya a kauyen.

A rikicin da ya barke, manoman sun yi zargin kona kadarori na Fulani makiyaya da suka hada da babura, kamar yadda rahotanni suka shaida wa DAILY POST.

Etsu Patigi, Alhaji Ibrahim Umar Bologi 11, ya shiga cikin rikicin yana mai kira ga al’ummarsa da su kwantar da hankalinsu tare da wanzar da zaman lafiya a yankin.

Ya kuma tabbatar wa Fulanin cewa babu wani ramuwar gayya da ‘yan uwansa za su yi, kuma babu abin da zai faru ga kowa, kamar yadda aka dawo da zaman lafiya.

Shugaban kungiyar Fulani ta Gan Allah reshen jihar Kwara, GAFDAN, Ali Muhammed Jounwuro, a martanin da ya mayar a Ilorin a ranar Asabar din da ta gabata ya bayyana matukar damuwarsa da cewa an kona akalla gidaje 103 na Fulanin da ba su ji ba ba su gani ba.

Ya tambayi dalilin da ya sa mutanen da aka zalunta su dauki doka a hannunsu idan suna zargin wasu suna aikata abin da bai dace ba.

“Sasanin Fulani sun fi shekara 40 a Rogu da ke karamar hukumar Patigi. Sun kasance masu bin doka da oda tsawon shekaru 40 ba tare da cutar da kowa ba,” shugaban ya kara da cewa.

Ya yi kira ga gwamnatin jihar Kwara da ta dauki matakin da ya dace kan lamarin domin kaucewa barkewar rikicin.

nigerian 
newspapers today the sun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp