fidelitybank

Makiyaya da Manona sun tayar da zaune tsaye a Kwara

Date:

Rikicin da ya barke tsakanin manoma da Fulani makiyaya a kauyen Rogu da ke karamar hukumar Patigi a jihar Kwara, ya yi sanadin mutuwar mutum guda.

DAILY POST ta tattaro cewa biyo bayan mutuwar manomin, wasu fulani manoma ne suka mamaye sansanin Fulani da ke kauyen.

Mamaya ya biyo bayan rikicin da ya barke tsakanin manoma da Fulani makiyaya a kauyen.

A rikicin da ya barke, manoman sun yi zargin kona kadarori na Fulani makiyaya da suka hada da babura, kamar yadda rahotanni suka shaida wa DAILY POST.

Etsu Patigi, Alhaji Ibrahim Umar Bologi 11, ya shiga cikin rikicin yana mai kira ga al’ummarsa da su kwantar da hankalinsu tare da wanzar da zaman lafiya a yankin.

Ya kuma tabbatar wa Fulanin cewa babu wani ramuwar gayya da ‘yan uwansa za su yi, kuma babu abin da zai faru ga kowa, kamar yadda aka dawo da zaman lafiya.

Shugaban kungiyar Fulani ta Gan Allah reshen jihar Kwara, GAFDAN, Ali Muhammed Jounwuro, a martanin da ya mayar a Ilorin a ranar Asabar din da ta gabata ya bayyana matukar damuwarsa da cewa an kona akalla gidaje 103 na Fulanin da ba su ji ba ba su gani ba.

Ya tambayi dalilin da ya sa mutanen da aka zalunta su dauki doka a hannunsu idan suna zargin wasu suna aikata abin da bai dace ba.

“Sasanin Fulani sun fi shekara 40 a Rogu da ke karamar hukumar Patigi. Sun kasance masu bin doka da oda tsawon shekaru 40 ba tare da cutar da kowa ba,” shugaban ya kara da cewa.

Ya yi kira ga gwamnatin jihar Kwara da ta dauki matakin da ya dace kan lamarin domin kaucewa barkewar rikicin.

punch news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...
X whatsapp