fidelitybank

Makiya ne suka kai hari Kogi – Gwamnati

Date:

Gwamnatin Kogi ta danganta fashewar wani abu da ya faru ranar Alhamis a Okene da “makiya” da suka yanke shawarar kai hari a ziyarar shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Mai baiwa Gwamna Yahaya Bello shawara kan harkokin tsaro, Jerry Omodara, ya zanta da Kamfanin Dillancin Labarai na (NAN) a Lokoja.

Fashewar ta faru ne da misalin karfe 9:00 na safe kusa da tsohon fadar na Ohinoyi na Ebiraland. Mutane hudu ne suka mutu.

Omodara ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar ta samu bayanan sirri game da lamarin.

Commodore mai ritaya ya ce, akwai isassun jami’an tsaro da za su kawo cikas ga “kokarin”.

“Makiya ci gaba sun yi kokarin kawar da hankalin shugaban kasa Muhammadu Buhari a ziyarar Kogi ta hanyar tayar da wannan fashewar.”

Omodara ya ci gaba da cewa “batattun ‘yan siyasa ne da mutanen da ba sa son wani abu mai kyau ga jiharsu” ne suka shirya fashewar.

Mashawarcin ya kara da zargin “‘yan siyasa da suka fusata” da yin murnar abin da ya faru.

Ya kuma bukaci kowa da kowa ya dauki tsaro da muhimmanci, yana mai gargadin cewa babu wanda ya tsira daga harin.

Majiyoyi sun shaidawa wakilin DAILY POST cewa an dasa bam a cikin wata mota kafin ya fashe.

legit.ng.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kashe kwamandan Boko Haram a tafkin Chadi

Sojojin Jamhuriyar Nijar sun sanar da kisan wani jagoran...

Hisbah za ta yi wa ‘yan Daban Kano aure

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta sanar da wani...

Ganduje ya dawo Najeriya bayan ya shafe wata guda a Landan

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Ganduje,...

Barrister Sa’idu ya kama aiki bayan ya maye gurbin Muhyi Magaji

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi sabon shugaba

Farfesa Haruna Musa, ya karɓi ragamar shugabancin jami’ar Bayero...

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa...

Gwamnatin Tinubu na takalar Kwankwaso da fada – Buba Galadima

Jigo a jam'iyyar NNPP, kuma na hannun tsohon gwamnan...

Newcastle United ta dauki dan wasan tsakiya Jacob daga Aston Villa

Newcastle United ta sanar da daukar dan wasan tsakiya...
X whatsapp