fidelitybank

Maki ya raba gardama tsakanin Arsenal da Tottenham

Date:

Arsenal da Tottenham sun tashi 2-2 a wasan mako na shida a gasar Premier League karawar hamayya ta kungiyoyin Arewacin Landan ranar Lahadi.

Arsenal ce ta fara cin kwallo ta hannun Cristian Romero, wanda ya ci gida a minti na 26 da take leda a Emirates, amma sauran minti uku hutu Heung-min Son ya farke.

Daga baya ne Gunners ta kara na biyu ta hannun Bukayo Saka a bugun fenariti, bayan da Romero ya taÉ“a kwallo da hannu a da’ira ta 18.

Kenan Romaro ya zama É—an wasa na 11 a Premier League da ya ci gida ya kuma jawo bugun fenariti, kuma shi ne na farko a Tottenham.

Minti É—aya tsakani da Arsenal ta ci kwallo, Tottenham ta farke ta hannun Heung-min Son, hakan ya sa sun raba maki a tsakaninsu a wasan hamayya.

Har yanzu ba a doke Gunners ba da fara kakar bana a Premier har da wanda ta caskara PSV Eindhoven 4-0 a Champions League ranar Laraba.

Wasa na biyu kenan da Gunners ta raba maki a babbar gasar tamaula ta Ingila, wadda ta fara yin 2-2 da Fulham a Emirates ranar 26 ga watan Agusta.

Ita ma dai Tottenham ba ta yi rashin nasara ba daga karawa shida da ta yi a Premier League ta kakar nan, wadda ta yi 2-2 a gidan Brentford ranar 13 ga watan Agusta

leadership news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp