Kwamishinan shari’a na jihar Kano, Barista Musa Abdullahi Lawan, ya bayyana cewa, Majalisar taimako ta sharia’a ta Najeriya ta bayyana bukata ta wakilci, Abdulmalik Tanko da sauran wadanda a ke zarginsu da kisan yarinya mai shekaru biyar, Hanifa Abubakar.
Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa, wannan ya biyo bayan umarnin mai shari’a, Usman Na’abba na babbar kotun jihar Kano ne a ranar 5 ga watan Fabrairu inda ya c,e jihar ta samarwa da Tanko da sauran mutum biyun lauya.
Lawan ya ce, duk wanda ke fuskantar shari’a kan zargin kisan kai, a na bukatar ya samu lauya, kuma idan mutum ba shi da lauya sannan ba shi da halin samowa, gwamnatin tarayya ta bukaci jiharsa da ta samar masa.
Ya yi bayanin cewa, Majalisar shari’ar ta Najeriya kafuwar gwamnatin tarayya ce wanda aikinsu ya kama da samar da lauya kyauta ga duk dan Najeriyan da bashi da lauya, kuma a ke zarginsa da kisan kai wanda hukuncinsa kai tsaye na kisa ne.
A na zargin Tanko da wasu mutum biyu da garkuwa tare da halaka Hanifa kuma shari’ar ta tsaya, saboda rashin lauyan wadanda ake zargin.
Bayan da alkali mai shari’a ya bayar da umarnin a samar musu da lauya, ya dage sauraron shari’ar zuwa ranar 14 ga watan Fabrairu mai zuwa.