fidelitybank

Makashin Hanifa da ake zargi ya samu Lauya – Gwamnatin Kano

Date:

Kwamishinan shari’a na jihar Kano, Barista Musa Abdullahi Lawan, ya bayyana cewa, Majalisar taimako ta sharia’a ta Najeriya ta bayyana bukata ta wakilci, Abdulmalik Tanko da sauran wadanda a ke zarginsu da kisan yarinya mai shekaru biyar, Hanifa Abubakar.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa, wannan ya biyo bayan umarnin mai shari’a, Usman Na’abba na babbar kotun jihar Kano ne a ranar 5 ga watan Fabrairu inda ya c,e jihar ta samarwa da Tanko da sauran mutum biyun lauya.

Lawan ya ce, duk wanda ke fuskantar shari’a kan zargin kisan kai, a na bukatar ya samu lauya, kuma idan mutum ba shi da lauya sannan ba shi da halin samowa, gwamnatin tarayya ta bukaci jiharsa da ta samar masa.

Ya yi bayanin cewa, Majalisar shari’ar ta Najeriya kafuwar gwamnatin tarayya ce wanda aikinsu ya kama da samar da lauya kyauta ga duk dan Najeriyan da bashi da lauya, kuma a ke zarginsa da kisan kai wanda hukuncinsa kai tsaye na kisa ne.

A na zargin Tanko da wasu mutum biyu da garkuwa tare da halaka Hanifa kuma shari’ar ta tsaya, saboda rashin lauyan wadanda ake zargin.

Bayan da alkali mai shari’a ya bayar da umarnin a samar musu da lauya, ya dage sauraron shari’ar zuwa ranar 14 ga watan Fabrairu mai zuwa.

taraba state today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi É—an shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin Æ´an Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taÉ“a barin Iran ta Æ™era makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaÆ™i – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama É—an kasar China da zargin kai wa Æ´an Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp