fidelitybank

Majalisar zartarwa ta ayyana sufuri kyauta na kusan wata guda

Date:

Majalisar zartarwar ƙarƙashin jagorancin shugaban ƙasa, Bola Tinubu ta sanar da cewa za ta tafi hutu daga ranar 18 ga watan Disamban 2024 zuwa 6 ga watan Janairun 2025.

Majalisar ta bayyana hakan ne bayan wata tattaunawa da ta gudanar yau Litinin a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

A bayanin bayan taron majalisar, hakan na nufin ba za a gudanar da wani taron majalisar ba a tsawon lokacin da za ta kwashe tana hutu.

Majalisar zartaswar Najeriya ta ƙunshi shugaban ƙasa da mataimakinsa da kuma ministoci.

Sanarwar da majalisar ta fitar ta nuna cewa a taron na yau Litinin ta kuma tattauna batun kasafin kuɗin shekarar 2025, da shugaban ƙasar zai gabatar a zauren Majalisar dokokin ƙasar.

Sufuri kyauta:

Majalisar zartaswar ta kuma ayyana sufuri kyauta ga ƴan ƙasar daga ranar 20 ga watan Disamba, 2024 zuwa 5 ga watan Janairun 2025 zuwa sassa daban-daban na ƙasar, kamar yadda gwamnati ta saba yi a lokacin “bukukuwan Sallah da na Kirisimeti.”

Sauya sunan jami’ar Abuja:

“Majalisar ta kuma amince da sauya sunan Jami’ar Abuja zuwa sunan tsohon shugaban ƙasar mulkin soji, Janar Yakubu Gowon, matakin da majalisar ta ce za ta gabatar gaban majalisar dokokin ƙasar domin neman amincewa.”

naija news today legits

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp