fidelitybank

Majalisar Wakilan Najeriya ta mayar wa da Kamfanin Binance na Kirifto martani

Date:

Majalisar Wakilan Najeriya ta ce iƙirarin cin hanci da jami’in kamfanin Binance, Tigran Gambaryan ya ce wasu jami’ai a ƙasar sun buƙata daga gare shi – ba komai ba ne illa ɓata wa hukumomin ƙasar suna.

Mista Gambaryan, ya yi zargin cewa wasu ƴan majalisar wakilan ƙasar sun nemi ya ba su cin hancin dala miliyan 150 a lokacin da aka samu wata kiki-kaka tsakanin gwamnatin Najeriya da kamfanin Binance, lamarin da ya sa hukumomin Najeriya suka tsare Mista Gambaryan.

Cikin wata sanarwar da majalisar wakilan ta fitar, ta hannun mai magana da yawunta, Hon. Akin Rotimi,ta ce ”an yi zarge-zargen – waɗanda a shekarar da ta gabata ma an yi ta yawo da su – an yi ne domin ɓata wa wasu ƴan majalisar suna ba wai majalisar gaba ɗaya ba”.

“Majalisa na kira ga ƴan ƙasa su yi watsi da zarge-zargen marasa tabbas da aka ƙirƙira da nufin ɓata wa hukomomi da wasu jami’an ƙasar suna”, kamar yadda sanarwar ta yi ƙarin haske.

Majalisar ta kuma wanke ƴanmajalisaun da Mista Gambaryan ya ambata cikin zarge-zargen nasa.

“Ƴan majalisunj da aka ambata cikin zargin, sun tabbatar da jagorancin majalisa cewa babu wani abu makamancin zargin da ya auku tsakaninsu da mista Gambaryan, kamar yadda ya yi zargin”.

Kan haka ne sanarwar ta ce, ƴan majalisun za su ɗauki matakin shari’a kan Mista Gambaryan.

”Ɗaya daga ciki ma tuni ya shigar da ƙara kotu domin wanke kansa, yayin da aka ƙarfafa wa sauran biyun gwiwa su ma su yi hakan,” in ji sanarwar.

A kwanakin baya ne aka gurfanar da Gambaryan- ɗan Amurka a kotun Najeriya bisa zargin laifukan kuɗi.

To sai dai hukumomin Najeriya sun sake shi ne bayan shiga tsakani da gwamnatin Amurka ta yi.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X a baya-bayan nan, Gambaryan ya yi ikirarin cewa kama shi da gwamnatin Najeriya ta yi ba bisa ƙa’ida ba ya sa tsohon shugaban ƙasar Amurka, Joe Biden ya kauce wa ganawar da ya shirya yi da Shugaban Najeriya, Bola Tinubu a yayin taron Majalisar Dinkin Duniya na 2024 (UNGA).

Ya kuma zargi mai baiwa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu kan lamarin, sannan ya ce gwamnatin Amurka ta rage yawan wakilan Najeriya da suka halarci taron na MDD.

Tuni dai gwamnatin Tinubu ta mayar masa ta martani kan zarge-zargen, tana mai cewa ba su da tushe balle makama, tana mai bayyana su da tsantar ƙarya da ya shirya kuma da gangan.

www.leadership ng.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp