fidelitybank

Majalisar Wakilai za ta yi bincike kan batun sojan ruwa Seaman Abbas

Date:

Kwamitin sojin ruwa na majalisar wakilan Najeriya ya ce zai yi bincike dangane da tsare sojan ruwan nan Seaman Abbas Haruna na tsawon shekaru shida ba “bisa ƙa’ida” ba.

Wata sanarwa da shugaban kwamitin, Yusuf Adamu Gagdi ya wallafa a shafinsa na X, ta ce “an tsare Seaman Abbas Haruna ne bisa umarnin wani babban soja Birgediya Janar M.S Adamu. Saboda haka kwamitin zai bincika domin tabbatar da cewa duk waɗanda ke da hannu a al’amarin sun fuskanci hukunci daidai abin da suka aikata.”

Yusuf Gagdi ya ƙara da cewa “rashin imanin da aka nuna a kan sojan ruwan saboda ɗan saɓanin da aka samu tsakaninsa da babbansa ya sa mutane da dama sun zubar da hawaye a lokacin da mai ɗakinsa ke bayar da bahasin yadda a al’amarin ya faru a gidan rediyo da talbijin na Brekete.”

Da ma dai hedikwatar tsaron Najeriya ma ta ce ta ga wani bidiyo da ke yawo na zargin tsare wani sojan ruwa mai suna Seaman Abbas Haruna tsawon shekaru shida kuma tana bincike a kai.

Hedikwatar rundunar tsaron ta Najeriya a wata sanarwa mai sa hannun kakainta, Birgediya Janar Tukur Gusau ta “muna bai wa al’ummar Najeriya tabbacin cewa rundunar tsaron Najeriya a shirye take ta samar da adalci da daidaito bisa dokokin ƙasa.

latest nigeria newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp