Majalisar Wakilan ta ƙasa ta yanke shawarar ɗaukaka ƙara kan hukuncin da Kotun Tarayya ta yi na bai wa Ministan Shari’a Abubakar Malami umarnin goge sashe na 84(12) na Dokar Zaɓe ta 2022.
Majalisar ta nemi ministan shari’ar kuma antoni janar da ya dakatar da aiwatar da umarnin har sai an kammala ɗaukaka ƙarar.
Ita ma Majalisar Dattawa ta ce, za ta ɗaukaka ƙarar bayan sanatoci da dama sun bijiro da buƙatar yin hakan a zamansu na yau Laraba.
Kakakin Majalisa Femi Gbajabiamila ya koka kan dalilin da ya sa aka kai ƙarar kotun da ke Jihar Abiya a Kudancin Najeriya, ya na mai cewa “majalisa ce kaɗai ke da ikon sauyawa ko yin doka a kundin tsarin mulkin Najeriya”.
Wakilin BBC da ya halarci zaman a Majalisar Dattawa ya ce, an samu ‘yar hatsaniya a lokacin da Sanata Sani Musa daga Jihar Neja ya buƙaci a cire sunansa daga jerin waɗanda suka amince a ɗaukaka ƙarar.
Sanatan da ke wakiltar mazaɓar Neja ta Tsakiya na cikin ‘yan takarar neman shugabancin jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya a zaɓen da a gudanar ranar 26 ga watan Maris.