fidelitybank

Majalisar wakilai za ta ɗaukaka ƙara a kan goge sashi na 84 a dokar Zaɓe

Date:

Majalisar Wakilan ta ƙasa ta yanke shawarar ɗaukaka ƙara kan hukuncin da Kotun Tarayya ta yi na bai wa Ministan Shari’a Abubakar Malami umarnin goge sashe na 84(12) na Dokar Zaɓe ta 2022.

Majalisar ta nemi ministan shari’ar kuma antoni janar da ya dakatar da aiwatar da umarnin har sai an kammala ɗaukaka ƙarar.

Ita ma Majalisar Dattawa ta ce, za ta ɗaukaka ƙarar bayan sanatoci da dama sun bijiro da buƙatar yin hakan a zamansu na yau Laraba.

Kakakin Majalisa Femi Gbajabiamila ya koka kan dalilin da ya sa aka kai ƙarar kotun da ke Jihar Abiya a Kudancin Najeriya, ya na mai cewa “majalisa ce kaɗai ke da ikon sauyawa ko yin doka a kundin tsarin mulkin Najeriya”.

Wakilin BBC da ya halarci zaman a Majalisar Dattawa ya ce, an samu ‘yar hatsaniya a lokacin da Sanata Sani Musa daga Jihar Neja ya buƙaci a cire sunansa daga jerin waɗanda suka amince a ɗaukaka ƙarar.

Sanatan da ke wakiltar mazaɓar Neja ta Tsakiya na cikin ‘yan takarar neman shugabancin jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya a zaɓen da a gudanar ranar 26 ga watan Maris.

daily post nigeria today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp