fidelitybank

Majalisar wakilai ta jingine ƙudurin ɗaure masu zanga-zanga ba bisa ƙa’ida ba

Date:

Shugaban Majalisar Dokoki, Tajudeen Abbas, ya sanar da janye ƙudurin da ya gabatar na samar da dokar ‘hukunta masu ayyukan tayar da hargitsi da waɗanda suka ƙi rera taken ƙasa’, wanda ya gabatar a zauren majalisar.

Wannan matakin na zuwa ne bayan lamarin ya janyo ce-ce-ku-ce da suka mai zafi tsakanin ƴan Najeriya, musamman matasa.

Matasan sun yi zargin cewa ana ƙoƙarin ɓullo da dokar ne domin murƙushe duk wani yunƙuri na yin zanga-zanga, bayan zanga-zangar matsin rayuwa da al’ummar ƙasar suka gudanar a farkon wannan wata na Agusta.

Shugaban Majalisar wakilan Najeriya, Tajudeen Abbas ne ya gabatar da dokar, mai taken ‘Counter Subversion Bill 2024’ a ranar 23 ga watan Yuli, inda ƙudurin ya tanadi hukunce-hukunce ga mutanen da aka kama da laifin zagon ƙasa ko tayar da hankali ko alaƙa da wasu ƙungiyoyin da aka haramta.

Wani ɓangare na dokar ya tanadi cewa: ‘Duk mutumin da aka kama da laifin yin karan-tsaye ga zirga-zirgar ababen hawa, ko datse hanya ko ƙaƙaba dokar zaman gida, ko yin tattaki ba bisa ƙa’ida ba ko kuma wasu abubuwa masu kamanceceniya da hakan zai fuskanci tarar naira miliyan biyu ko kuma ɗaurin shekara biyar a gidan yari.’

Haka nan wani ɓangare na ƙudurin dokar da ya ja hankalin al’umma shi ne wanda ya ce: ‘Duk wani mutum da ya lalata wani tambari na ƙasa, ko ya ƙi rera taken ƙasa, ko ya yi ƙoƙarin lalata wurin ibada da nufin haifar da rikici da yi wa gwamnati ɓarna, ya aikata laifi wanda za a buƙace shi ya biya tarar naira miliyan biyar ko zaman gidan yari na shekara 10.’

A cikin sanarwar janye ƙudurin dokar, wadda ta samu sa hannun mai taimaka wa shugaban Majalisar wakilan kan yaɗa labarai, Musa Abdullahi Krishi, ta ce an janye dokar ne “bayan tattaunawa mai zurfi da masu ruwa da tsaki da kuma kyakkyawan la’akari da halin da ƙasa ke ciki.”

Sanarwar ta ƙara da cewa Honorabul Abbas “ba zai taɓa goyon bayan duk wani mataki da zai yi illa ga zaman lafiya da haɗin kan al’ummar ƙasar ba.”

Zanga-zangar da wasu ƴan ƙasar suka gudanar a cikin wannan wata na Agusta ya rikiɗe zuwa rikici a wasu jihohin ƙasar.

Yunƙurin da hukumomi suka yi na killace masu zanga-zanga a wani keɓeɓɓen wuri a biranen Abuja da Legas ya janyo taƙaddama tsakanin masu zanga-zangar da jami’an tsaro.

Haka nan hatsaniyar da ta faru, bayan mutane sun tare hanyoyi a da yin tattaki a wasu birane kamar Kano da Kaduna sun haifar da taƙaddamar da ake zargin ta janyo asarar rayuka da dukiya mai yawa.

vgn news today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp