fidelitybank

Majalisar wakilai ta jingine ƙudurin ɗaure masu zanga-zanga ba bisa ƙa’ida ba

Date:

Shugaban Majalisar Dokoki, Tajudeen Abbas, ya sanar da janye ƙudurin da ya gabatar na samar da dokar ‘hukunta masu ayyukan tayar da hargitsi da waɗanda suka ƙi rera taken ƙasa’, wanda ya gabatar a zauren majalisar.

Wannan matakin na zuwa ne bayan lamarin ya janyo ce-ce-ku-ce da suka mai zafi tsakanin ƴan Najeriya, musamman matasa.

Matasan sun yi zargin cewa ana ƙoƙarin ɓullo da dokar ne domin murƙushe duk wani yunƙuri na yin zanga-zanga, bayan zanga-zangar matsin rayuwa da al’ummar ƙasar suka gudanar a farkon wannan wata na Agusta.

Shugaban Majalisar wakilan Najeriya, Tajudeen Abbas ne ya gabatar da dokar, mai taken ‘Counter Subversion Bill 2024’ a ranar 23 ga watan Yuli, inda ƙudurin ya tanadi hukunce-hukunce ga mutanen da aka kama da laifin zagon ƙasa ko tayar da hankali ko alaƙa da wasu ƙungiyoyin da aka haramta.

Wani ɓangare na dokar ya tanadi cewa: ‘Duk mutumin da aka kama da laifin yin karan-tsaye ga zirga-zirgar ababen hawa, ko datse hanya ko ƙaƙaba dokar zaman gida, ko yin tattaki ba bisa ƙa’ida ba ko kuma wasu abubuwa masu kamanceceniya da hakan zai fuskanci tarar naira miliyan biyu ko kuma ɗaurin shekara biyar a gidan yari.’

Haka nan wani ɓangare na ƙudurin dokar da ya ja hankalin al’umma shi ne wanda ya ce: ‘Duk wani mutum da ya lalata wani tambari na ƙasa, ko ya ƙi rera taken ƙasa, ko ya yi ƙoƙarin lalata wurin ibada da nufin haifar da rikici da yi wa gwamnati ɓarna, ya aikata laifi wanda za a buƙace shi ya biya tarar naira miliyan biyar ko zaman gidan yari na shekara 10.’

A cikin sanarwar janye ƙudurin dokar, wadda ta samu sa hannun mai taimaka wa shugaban Majalisar wakilan kan yaɗa labarai, Musa Abdullahi Krishi, ta ce an janye dokar ne “bayan tattaunawa mai zurfi da masu ruwa da tsaki da kuma kyakkyawan la’akari da halin da ƙasa ke ciki.”

Sanarwar ta ƙara da cewa Honorabul Abbas “ba zai taɓa goyon bayan duk wani mataki da zai yi illa ga zaman lafiya da haɗin kan al’ummar ƙasar ba.”

Zanga-zangar da wasu ƴan ƙasar suka gudanar a cikin wannan wata na Agusta ya rikiɗe zuwa rikici a wasu jihohin ƙasar.

Yunƙurin da hukumomi suka yi na killace masu zanga-zanga a wani keɓeɓɓen wuri a biranen Abuja da Legas ya janyo taƙaddama tsakanin masu zanga-zangar da jami’an tsaro.

Haka nan hatsaniyar da ta faru, bayan mutane sun tare hanyoyi a da yin tattaki a wasu birane kamar Kano da Kaduna sun haifar da taƙaddamar da ake zargin ta janyo asarar rayuka da dukiya mai yawa.

sahara hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp