Majalisar wakilai kasa ta sanar da cewa ta janye hukuncin da ta dauka kan wasu kudurin doka uku da suka shafi mata da aka sake gabatar ma ta.
Kudurorin dokar sun hada da na zama dan kasa, da na zama asalin dan wata jiha a Najeriya da na samar wa mata kashi 35 cikin 100 na mukaman siyasa.
Dukkan wadannan kudurorin dokan sun gaza tsallake bukatar doka da ta bukaci sai kason ‘yan majalisa biyu cikin ukunsu sun amince da su kafin a amince da su a gyaran da ake wa tsarin mulkin kasar.
Sanarwar da majalisar ta fitar ta ce, kakakin majalisar Femi Gbajabiamila da sauran ‘yan majalisar na son ganin an ci gaba da aiki kan kudurorin uku, kuma sun mika su ga babban kwamitin gidan domin a sake gabatar da su.
Sanarwar ta kuma ce, majalisar za ta fara aiki kan kudurorin uku tare da sauran kudurorin da ke gabanta nan da mako hudu mai zuwa. In ji BBC.