Majalisar wakilai ta ta magantu a kan yajin aikin da ASUU take yi a zaman farkon da ta yi a makon nan.
Honarabul Dozie Nwankwo ya koka a game da yadda malaman jami’o’i suke shiga yajin-aiki bini-bini.
Dan Majalisar na Anambra ya bada shawarar komawa tattaunawa da aka sa wa hannu domin a ceci dalibai.
Majalisar wakilan tarayya ta bukaci gwamnatin tarayya da kungiyar ASUU su yi aiki da yarjejeniyar sanyawa hannu ta MoU, a wajen shawo kan sabaninsu.
A cewar talabijin ta Channels, ‘yan majalisar tarayya sun nemi gwamnati da malaman jami’an su sasanta, domin albarkacin daliban kasar nan.