Majalisar zartaswar jihar Kano ta amince da aiwatar da wasu ayyukan bunkasa birane da kauyukan jihar.
Kwamishinan yada labarai na jihar, Kwamrade Muhammad Garba, wanda ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai, sakamakon taron mako-mako na majalisar da aka gudanar a dakin taro na Africa House dake gidan gwamnati Kano, ya ce, ayyukan sun hada da sake gina hanyar Kwanar Gogori da kuma kammala Kanye-Kabo da titin Dubagau road.
Ya ce, majalisar ta amince da ayyukan sun hada da na kwangilar samarwa da sanya kwalbati a gadar Tijjani Hashim (Galadiman Kano) ta Underpass akan kudi N525, 435, 750.00.
Garba ya bayyana cewa, majalisar ta amince da sake duba kiyasin kwangilar sanya duwatso na rufe bangon masu kyalli da santsi da ke karkashin titin gadar Panshekara da Madobi a kan kudi Naira miliyan 65, 709, 198.00.
Kwamishinan ya kuma bayyana cewa majalisar ta amince da bayar da kwangilar sake gina titin garin Gogori mai nisan kilomita 3.35 daga titin Shanono zuwa Gogori a karamar hukumar Bagwai kan kudi Naira miliyan 290, 265, 511.33.