A ranar Litinin ne Majalisar Dokokin Jihar Ribas ta gabatar da sanarwar rashin da’a da ake zargin Gwamnan Jihar, Siminalayi Fubara da mataimakiyarsa, Ngozi Odu.
A cewar Channels TV, ‘yan majalisar sun yi ikirarin a cikin sanarwar cewa matakin ya dace da kundin tsarin mulkin Najeriya.
Sanarwar ta kara da cewa, “A bisa bin sashe na 188 na kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya na shekarar 1999 (wanda aka yi wa kwaskwarima), da sauran wasu manyan dokoki, mu ‘yan majalisar dokokin jihar Ribas da muka rattaba hannu a kan mu, muna mika muku sanarwar rashin da’a da mataimakin gwamnan jihar Ribas ya yi wajen gudanar da ayyukan ofishinta.
Duk da cewa a baya majalisar ta musanta wani yunkuri na tsige Fubara, amma dai ana ta cece-kuce game da shirin tsige gwamnan.