Majalisar dokokin jihar Osun, ta sanar da shirin fara bincike kan bashin Naira biliyan 407.32 na jihar da gwamna Ademola Adeleke ya bayyana tun farko.
Nation ta tuna cewa Adeleke yayin da yake ganawa da Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Osun a ranar Alhamis ya bayyana cewa bashin Naira biliyan 407.32 ya ciyo magabacinsa, Adegboyega Oyetola yayin da ya sha alwashin yi masa tambayoyi kan bashin.
Sai dai Oyetola ya karyata maganar ta bakin mai taimaka masa kan harkokin yada labarai Ismail Omipidan cewa bai taba karbar wani lamuni ba tsawon shekara hudu amma gwamnatin Rauf Aregbesola ta ciwo bashin. Ya kalubalanci Adeleke da ya buga ranar da aka samu lamunin.
Hakazalika, Majalisar ta bakin Shugaban Kwamitin Yada Labarai da Watsa Labarai na Majalisar, Kunle Akande a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a ta nuna damuwarta kan bayyana bashin tare da bayyana cewa an fara bincike kan rancen da jihar ta samu.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Majalisar dokokin jihar Osun ta bayyana damuwarta kan yadda gwamnan jihar, Sanata Ademola Adeleke ya bayyana bayyana bashi a jiya.
“Majalisa a matsayin wakilan jama’a da aka amince da su ya zama wajibi ta nemi karin haske tare da sanar da jama’ar jihar yadda ya kamata.