Majalisar dokokin jihar Osun ta soke dokar rera taken jihar da rage tutar na dokar 2012.
An dai yi watsi da dokar ne yayin zaman majalisar a ranar Talata.
A cewar sanarwar da kakakin majalisar, Adewale Egbedun ya fitar, an dauki matakin ne bisa ga hukuncin da wata babbar kotun tarayya ta yanke a ranar 14 ga watan Disamba, 2017.
Kanmi Ajibola wanda yanzu ya zama dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar jihar Oriade, jam’iyyar PDP ne ya shigar da karar gaban kotu.
A cewar shugaban majalisar, “Duk da fahimtar cewa akwai wasu abubuwa na dokar da suka dace, majalisar ta amince da cewa duk gyare-gyaren da aka yi kan rera wakar taken jihar Osun, da yin kasa-kasa da Tuta na dokar 2012 na daga cikin kudirin dokar wakokin jihar Osun. Crest and Flag Bill 2023, wanda Shugaban Masu Rinjaye ya ɗauki nauyinsa.
“A zahiri, abin da majalisar ta yi, shi ne watsi da dokar da kotun da ke da hurumin shari’a ta riga ta soke ta, don samar da wata sabuwar doka da za ta mutunta harufa da ruhin kundin tsarin mulkin Najeriya da ya yi rantsuwar aiki. ”
Shugaban majalisar a ranar Juma’a ya sanar da majalisar a yayin zaman majalisar kan matakin soke dokar.
Majalisar ta zartas da dokar samar da waka, tuta da kuma karramawa ga jihar karkashin jagorancin kakakin majalisar Naheem Salam.
Gwamnatin Rauf Aregbesola ta yi wa jihar waka da tuta da kuma karramawa.
Har ila yau, gwamnatin ta canza sunan jihar daga “Jihar Osun, Jihar Rayayyar Rayuwa” zuwa “Jihar Osun, Jihar masu nagarta.”