fidelitybank

Majalisar dokokin Katsina ta gargaɗi MTN

Date:

Majalisar dokokin jihar Katsina ta buƙaci kamfanin sadarwa na MTN ya daina yawan katse sabis ba tare da yin gamsasshen bayani ga al’umma ba.

Majalisar ta bayyana cewa yawan katse sadarwar na cutar da kasuwanci da zamantakewar al’ummar jihar.

Cikin wani ƙudirin gaggawa da ɗan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Dandume, Hon. Yahaya Nuhu Mahuta ya gabatar a zauren Majalisar ranar Talata, ya ce katse sabis da kamfanin ke yi ya shafi ɓangarori kasuwanci, ilimi da harkokin yau-da-kullum na al’ummar jihar.

Mataimakin kakakin majalisar jihar, Honarabul Hon Abduljalal Haruna Runka ya shaida wa BBC cewa haƙƙin kamfanin ne ya samar da nagartattun ayyuka, domin al’umma kuɗi suka biya don neman biyan buƙata.

Ya bayyana cewa babban takaicin, kamfanin bashi bada wani uzuri ko cikakken bayani akan dalilin ɗaukewar sabis ɗin.

Hon. Mahuta ya ce al’umma suna da hakki a kan kamfanin, kuma gazawar zai baiwa alummar damar chanza tsarin da suke ganin zai taimake su.

Haka kuma majalisar na duba yiwuwar gayyato kamfanin domin yin gamsasshen bayani ga majalisar kan dalilin yin haka.

Mataimakin kakakin majalisar, ya umarci kwamitin sadarwa na majalisar ya aiwatar da bincike a kan koken, tare da kawo rahoto cikin mako biyu.

daily post today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp