fidelitybank

Majalisar dokokin Kano ta yi watsi da kudiri kan hukumar Zakka da Hubsi

Date:

Majalisar dokokin Kano taki amincewa da rahoton da kwamitin ta na addinai ya gabatar Mata akan sunayen mutanen da Gwamna Abba Kabir Yusif ya aike Mata domin tantancewa a nada su shugabancin hukumar Zakka da Hubusi da hukumar Shari’a na jihar nan.

Majalisar dokokin taki amincewa da rahoton ne biyo bayan tsokaci da Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Gezawa Abdullahi Yahaya tsamiyar Kara yayi, inda yace dokar data kafa hukumomin biyu tayi tanadin cewa dole ne a dakko Shugabannin hukumomin daga dukkan bangarorin jihar nan, tare da nada mutane 14 a matsayin mambobi bayan an samar da shugaba, mataimaki da manyan kwamishinoni na daya dana biyu a kowace hukuma.

Tsamiyar Kara yace Idan akayi duba na tsanaki akan sunayen da gwamnan ya turo karamar hukuma 1 kawai ta samu wakilcin mutane hudu a kowace hukuma, sannan wata hukumar mutane 9 aka turo wata Kuma aka turo mutum 10 domin tantancewar wanda hakan kai tsaye Karan tsaye ne a dokar data kafa hukumomin biyu.

Da yake Karin bayani akan batun, mataimakin Shugaban majalisar dokokin Mohd Bello butu-butu, yace Sanya kowane bangare na jihar nan a kunshin shugabancin hukumomin biyu zai tabbatar da adalci ta fuskar siyasa, tare da Kalubalantar bangaren masana doka na majalisar kan su dinga fahimtar kowane Sako aka kawo majalisar kafin a gabatar da shi a gaban ta.

A tasa gudunmawar daya bayar yayin Zaman ma yau shugaban masu rinjaye na majalisar Lawan Hussaini Dala yace majalisar taki amincewa da rahoton kwamitin ne kawai ba wai nagartar wadanda aka turo ba, sai dai ya bukaci gwamna Abba daya tabbatar da sahihancin wadanda yake nadawa mukamai kasancewar daga cikin wadanda gwamnan ya turo mutum hudu basu amsa gayyata majalisar ba.

besda salary

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp