fidelitybank

Majalisar dokokin Kano ta yi watsi da kudiri kan hukumar Zakka da Hubsi

Date:

Majalisar dokokin Kano taki amincewa da rahoton da kwamitin ta na addinai ya gabatar Mata akan sunayen mutanen da Gwamna Abba Kabir Yusif ya aike Mata domin tantancewa a nada su shugabancin hukumar Zakka da Hubusi da hukumar Shari’a na jihar nan.

Majalisar dokokin taki amincewa da rahoton ne biyo bayan tsokaci da Dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Gezawa Abdullahi Yahaya tsamiyar Kara yayi, inda yace dokar data kafa hukumomin biyu tayi tanadin cewa dole ne a dakko Shugabannin hukumomin daga dukkan bangarorin jihar nan, tare da nada mutane 14 a matsayin mambobi bayan an samar da shugaba, mataimaki da manyan kwamishinoni na daya dana biyu a kowace hukuma.

Tsamiyar Kara yace Idan akayi duba na tsanaki akan sunayen da gwamnan ya turo karamar hukuma 1 kawai ta samu wakilcin mutane hudu a kowace hukuma, sannan wata hukumar mutane 9 aka turo wata Kuma aka turo mutum 10 domin tantancewar wanda hakan kai tsaye Karan tsaye ne a dokar data kafa hukumomin biyu.

Da yake Karin bayani akan batun, mataimakin Shugaban majalisar dokokin Mohd Bello butu-butu, yace Sanya kowane bangare na jihar nan a kunshin shugabancin hukumomin biyu zai tabbatar da adalci ta fuskar siyasa, tare da Kalubalantar bangaren masana doka na majalisar kan su dinga fahimtar kowane Sako aka kawo majalisar kafin a gabatar da shi a gaban ta.

A tasa gudunmawar daya bayar yayin Zaman ma yau shugaban masu rinjaye na majalisar Lawan Hussaini Dala yace majalisar taki amincewa da rahoton kwamitin ne kawai ba wai nagartar wadanda aka turo ba, sai dai ya bukaci gwamna Abba daya tabbatar da sahihancin wadanda yake nadawa mukamai kasancewar daga cikin wadanda gwamnan ya turo mutum hudu basu amsa gayyata majalisar ba.

nigeria daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...
X whatsapp