fidelitybank

Majalisar dokokin Kano ta taya Kiristoci murnar Kirsimeti

Date:

Majalisar dokokin Kano ta bukaci mabiya addinin kirista da suyi amfani da lokutan bukukuwan kirsimeti da sabuwar shekara wajen mayar da hankali domin yin addu’o’in samun saukin matsin rayuwar da ake ciki a kasar nan.

Shugaban majalisar Jibril Isma’il Falgore ne ya bayyana hakan ta cikin sakon taya murna daya aike ga mabiya addinin kiristar dake kasar nan.

Falgore, ta bakin babban sakataren yada labaran Majalisar dokokin ta Kano, Kamaluddeen Sani Shawai ya ce sakon majalisar wata alama ce ta kyakyyawar mu’amalar dake tsakanin mabiya addinai daban-daban a kasar nan.

Falgore ya kuma bukaci mabiya addinin na kirista dake jihar nan da su ci gaba da ba wa gwamnati da Majalisar dokokin ta Kano cikakken hadin kai da goyon bayan daya dace domin ciyar da Kano gaba da kowace fuska.

Kakakin majalisar Falgore ya kara jaddada kudurin su na cigaba da marawa gwamnatin jiha baya akan dukkan manufofinta wadanda suke nufin samar da kyakkawan muhallin rayuwa ga kowa ba tare da banbancin addini ko kabila ba.

punch newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...
X whatsapp