fidelitybank

Majalisar dokokin Kano ta taya Kiristoci murnar Kirsimeti

Date:

Majalisar dokokin Kano ta bukaci mabiya addinin kirista da suyi amfani da lokutan bukukuwan kirsimeti da sabuwar shekara wajen mayar da hankali domin yin addu’o’in samun saukin matsin rayuwar da ake ciki a kasar nan.

Shugaban majalisar Jibril Isma’il Falgore ne ya bayyana hakan ta cikin sakon taya murna daya aike ga mabiya addinin kiristar dake kasar nan.

Falgore, ta bakin babban sakataren yada labaran Majalisar dokokin ta Kano, Kamaluddeen Sani Shawai ya ce sakon majalisar wata alama ce ta kyakyyawar mu’amalar dake tsakanin mabiya addinai daban-daban a kasar nan.

Falgore ya kuma bukaci mabiya addinin na kirista dake jihar nan da su ci gaba da ba wa gwamnati da Majalisar dokokin ta Kano cikakken hadin kai da goyon bayan daya dace domin ciyar da Kano gaba da kowace fuska.

Kakakin majalisar Falgore ya kara jaddada kudurin su na cigaba da marawa gwamnatin jiha baya akan dukkan manufofinta wadanda suke nufin samar da kyakkawan muhallin rayuwa ga kowa ba tare da banbancin addini ko kabila ba.

nigerianewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp