Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya ta Majalisar Ɗinkin Duniya (IAEA), in ji rahotanni daga kafafen yaɗa labaran gwamnati.
Shugaban majalisar, Mohammad Bagher Ghalibaf, ya ce hukumar IAEA ta gaza yin Allah-wadai da hare-haren da Isra’ila da Amurka suka kai kan wuraren nukiliyar Iran, lamarin da ya sa majalisar dokokin Iran ɗin ta yanke wannan shawarar.
Ghalibaf ya ce hukumomin nukiliya na Iran za su “dakatar da haɗin kai da IAEA har sai an tabbatar da tsaron wuraren da ake sarrafa makamashin nukiliya”.
Ya kuma ƙara da cewa shirin Iran na nukiliya “zai ci gaba da tafiya cikin sauri da aminci”.
Amma kuma wannan ƙuri’ar da aka kaɗa, sai an samu amincewa daga manyan jagororin gwamnati kafin ta zama doka a hukumance.