Majalisar Dinkin Duniya ta bi sahun Tarayya Turai na yin Allah-wadai da mayakin da Twitter ya dauka na rufe shafin wasu ‘yan jarida.
Twitter ya rufe shafin ‘yan jaridar New YYork Times da na CNN da kuma na Washington Post.
MDD ta aike da sakon Twitter kan cewa ‘yancin kafafen yada labrai ba “abin wasa ba ne” yayin da Tarayyar Turai ta yi gargadin dakatar da kamfanin.
Kakakin Kamfanin Twitter ya shaidawa kamfanin yada labarai na Amurka cewa an dakatar da shafukan nasu ne kan abin da ke da alaka bayyana wasu bayanai kan inda wani abu yake.