fidelitybank

Majalisar Dinkin Duniya ta yi Allah wadai da Boko Haram

Date:

Majalisar Dinkin Duniya ta yi Allah wadai da sace ‘yan gudun hijira masu yawa a yankin arewa maso gabashin Najeriya.

Rahotonni sun ce akallah ‘yan gudun hijira 200 ne galibinsu mata da ƙananan yara da ‘yan mata mayaƙan Boko Haram suka yi garkuwa da su a ƙarshen mako, kodayake har yanzu a hukumance ba a tabbatar da aadin mutanen ba.

Mayaƙan sun saki wasu tsoffin mata da ƙananna yara ‘yan kasa da shekara 10.

Cikin wata sanarwar da ta fitar ranar Laraba, Majalisar Dinkin Duniyar ta bakin kodinetan ayyukan jin ƙai a Najeriya, Mohammed Malick Fall, ya ce sace mutanen masu yawa, ”tunatarwa ce cewa mata da ‘yan mata na daga cikin mutanen da ke ciki hatsarin harin mayaƙan Boko Haram a yankin arewa maso gabashin ƙasar.

Ya ƙara da cewa lamarin ya faru ne a makon da ya gabata a lokacin da ‘yan gudun hijirar suka tafi neman itacen girki.

yayin da yake jajanta wa iyalan ‘yan uwan waɗanda lamarin ya shafa, Mista Malik Fall ya buƙaci hukumomi su samar wa mazauna sansanonin gudun hijira sana’o’i da ayyukan yi don rage hatsarin da suke ciki.

Aƙalla mutum 40,000 ne aka kashe tare da raba fiye da miliyan biyu da muhallansu cikin fiye da shekara 10 na yakin Boko Haram.

Mazauna sansanonin ‘yan gudun hijira na fama da ƙarancin abinci, Inda ake kashe su ko sace su tare da tilasta musu shiga ƙungiyoyin masu dauke da makamai idan suka yi yunƙurin zuwa gonakinsu ko neman abinci.

Haka kuma a wasu lokuta mayaƙan kan ci zarafinsu, inda suke tilasta musu auren mayaƙan.

bbc news nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp