Majalisar Dinkin Duniya ta kakaba takunkumai a kan manyan jami’an gwamnatin Liberia kan zarge-zargen Rashawa.
Cikin mutanen da takunkuman ya shafa akwai, Nathaniel McGill, wanda shi ne ministan harkokin fadar gwamnati kuma shugaban ma’aikatan gwamnati na shugaba George Weah.
Wata sanarwar ma’aikatar baitul-malin Amurka ta zargi Mista McGill, da karbar toshiya wajen bada ayyukan gwamnati. A cewar BBC.
Shi ma Antoni-Janar na Liberia, Sayma Syrenius Cephus, da shugaban hukumar kula da tashoshin jiragen ruwa ta kasa, Bill Twehway, an rike asusun bankunansu da kadarorinsu da ke Amurka.
‘Yan Liberia sun zuba ido domin ganin irin matakin da shugaba George Weah, zai dauka kan wadannan jami’ai nasa.