fidelitybank

Majalisar Dattawa za ta samar da dokokin rage illar bala’o’i – Sanatocin Arewa

Date:

Majalisar dattawa na shirin samar da wasu dokoki da nufin rage illar bala’o’in muhalli kamar su ambaliyar ruwa a ƙasar.

Hakan ya biyo bayan ambaliyar ruwa da ta yi ɓarna a Maiduguri babban birnin jihar Borno a ranar Talata bayan rushewar madatsar ruwa ta Alau.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban Sanatoci na yakin Arewa, Abdulaziz Musa Yar’adua ya fitar ranar Alhamis a Abuja kamar yadda Jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Shugaban ya ce, “Majalisar Dattawa za ta ci gaba da aiwatar da dokoki da tsare-tsare da za su daƙile illolin bala’o’in muhalli da kuma samar da ci gaba mai dorewa.”

“Muna goyon bayan al’ummar jihar Borno tare da tabbatar musu da goyon bayanmu a wannan mawuyacin lokaci.”

Sanarwar ta buƙaci gwamnatocin jihohi 36 na tarayyar ƙasar da su tsara manyan tsare-tsare don tunkarar matsalar sauyin yanayi a wani ɓangare na ƙoƙarin daƙile bala’o’in muhalli kamar su ambaliyar ruwa.

Sanarwar ta kuma yaba wa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu kan amincewa da Naira biliyan 3 a matsayin asusun shiga tsakani ga wadanda bala’in ya rutsa da su tare da jajanta wa gwamnati da al’ummar jihar Borno dangane da ambaliyar ruwa da ta yi sanadiyar mutuwar mutane da dama da lalata gidaje da gonaki.

legit ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp