Majalisar dattawa na shirin samar da wasu dokoki da nufin rage illar bala’o’in muhalli kamar su ambaliyar ruwa a ƙasar.
Hakan ya biyo bayan ambaliyar ruwa da ta yi ɓarna a Maiduguri babban birnin jihar Borno a ranar Talata bayan rushewar madatsar ruwa ta Alau.
Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban Sanatoci na yakin Arewa, Abdulaziz Musa Yar’adua ya fitar ranar Alhamis a Abuja kamar yadda Jaridar Daily Trust ta ruwaito.
Shugaban ya ce, “Majalisar Dattawa za ta ci gaba da aiwatar da dokoki da tsare-tsare da za su daƙile illolin bala’o’in muhalli da kuma samar da ci gaba mai dorewa.”
“Muna goyon bayan al’ummar jihar Borno tare da tabbatar musu da goyon bayanmu a wannan mawuyacin lokaci.”
Sanarwar ta buƙaci gwamnatocin jihohi 36 na tarayyar ƙasar da su tsara manyan tsare-tsare don tunkarar matsalar sauyin yanayi a wani ɓangare na ƙoƙarin daƙile bala’o’in muhalli kamar su ambaliyar ruwa.
Sanarwar ta kuma yaba wa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu kan amincewa da Naira biliyan 3 a matsayin asusun shiga tsakani ga wadanda bala’in ya rutsa da su tare da jajanta wa gwamnati da al’ummar jihar Borno dangane da ambaliyar ruwa da ta yi sanadiyar mutuwar mutane da dama da lalata gidaje da gonaki.