Majalisar dattawa za ta dawo zamanta na shekarar 2023 a ranar 17 ga watan Janairu bayan zamanta na ranar Laraba 28 ga Disamba, 2022.
Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan ne ya sanar da hakan yayin zaman da ‘yan majalisar suka yi a yau, inda ‘yan majalisar suka yi muhawara kan bukatar shugaban kasa Muhammadu Buhari na a duba bukatar hanyoyin da za a samu ci gaba.
Buhari dai ya mika wa majalisar kunshin kasafin kudi, domin su duba tare da ratta a hannu a kai.