fidelitybank

Majalisar Dattawa na neman a yi dokar ɗaure Iyayen da suka ƙi kai ‘Ya’Yansu makaranta

Date:

Majalisar dattawan Najeriya ta ce tana son yi wa kundin tsarin mulkin ƙasar gyara fuska, ta yadda za a samar da dokar hukuncin ɗauri ga iyayen da suka ƙi sanya ‘ya’yansu a makaranta.

Shugaban kwamitin ilimi na majalisar, Sanata Lawan Adamu Usman ya ce majalisar na duba yiwawar sanya hukunci ɗaurin wata shida ga duk iyayen da suka kasa sanya ‘ya’yansa a makaranta.

Yayin da yake zantawa da manema labarai, bayan gabatar da rahoton kwamitinsa a gaban majalisar a ranar Laraba, Sanata Lawan ya ce “muna son a yi dokar ɗaurin wata shida ga iyayen da suka ƙi sanya ‘ya’yansu a makaranta. Shi ma ilimi masu iya magana na cewa shi ne gishirin rayuwa, kuma shi ne maganin duka matsalolin da ke faruwa a ƙasar nan,” in ji sanatan.

Tun da farko shugaban Majalisar Dattawan, Sanata Godswill Akpabio ya ce akwai yara fiye da miliyan 20 da ba sa zuwa makaranta a Najeriya, waɗanda ya ce idan ba a ɗauki matakin kula da su ba, za su iya zama ɓata-gari idan suka girma.

Shi ma Mataimakain Shugaban Majalisar, Sanata Barau Jibrin ya ce matsalar rashin zuwan yara makaranta, babbar damuwa ce ga ƙasar, wanda ya ce ta fi ƙamari musamman a yankin arewacin ƙasar.

today nation

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp