fidelitybank

Majalisar Dattawa na neman a yi dokar ɗaure Iyayen da suka ƙi kai ‘Ya’Yansu makaranta

Date:

Majalisar dattawan Najeriya ta ce tana son yi wa kundin tsarin mulkin ƙasar gyara fuska, ta yadda za a samar da dokar hukuncin ɗauri ga iyayen da suka ƙi sanya ‘ya’yansu a makaranta.

Shugaban kwamitin ilimi na majalisar, Sanata Lawan Adamu Usman ya ce majalisar na duba yiwawar sanya hukunci ɗaurin wata shida ga duk iyayen da suka kasa sanya ‘ya’yansa a makaranta.

Yayin da yake zantawa da manema labarai, bayan gabatar da rahoton kwamitinsa a gaban majalisar a ranar Laraba, Sanata Lawan ya ce “muna son a yi dokar ɗaurin wata shida ga iyayen da suka ƙi sanya ‘ya’yansu a makaranta. Shi ma ilimi masu iya magana na cewa shi ne gishirin rayuwa, kuma shi ne maganin duka matsalolin da ke faruwa a ƙasar nan,” in ji sanatan.

Tun da farko shugaban Majalisar Dattawan, Sanata Godswill Akpabio ya ce akwai yara fiye da miliyan 20 da ba sa zuwa makaranta a Najeriya, waɗanda ya ce idan ba a ɗauki matakin kula da su ba, za su iya zama ɓata-gari idan suka girma.

Shi ma Mataimakain Shugaban Majalisar, Sanata Barau Jibrin ya ce matsalar rashin zuwan yara makaranta, babbar damuwa ce ga ƙasar, wanda ya ce ta fi ƙamari musamman a yankin arewacin ƙasar.

naija legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp