Takarar shugabancin jam’iyyar APC mai mulki ta kasa ta sake daukar wani sabon salo, yayin da majalisar dattawa ta karyata rahotannin da kafafen yada labarai suka yada kan amincewa da Sanata Abdullahi Adamu kan mukamin.
Sanata Ajibola Basiru, shugaban kwamitin majalisar dattawa mai kula da harkokin yada labarai da hulda da jama’a ne ya bayyana haka yayin ganawa da manema labarai ranar Litinin a Abuja.
Sanatoci uku; Abdullahi Adamu, Sani Musa da Tanko Al-Makura sun fafata ne a zaben shugaban jam’iyyar APC na kasa a babban taron kasa na ranar 26 ga Maris.
Sai dai rahotanni daga jam’iyyar sun nuna cewa, Adamu ne dan takarar shugaban kasa Muhammadu Buhari.
A cikin bayanin nasa, Basiru ya bayyana cewa, majalisar dattawan ba ta amince da wani dan takara a wannan matsayi ba.