Majalisar dattawa ta shirya wani zaman gaggawa a yau Laraba, a daidai lokacin da ake shirin gudanar da zanga-zangar a fadin kasar.
Wata takardar cikin gida daga magatakardar majalisar dattawa ta ce, shugaban majalisar, Godswill Obot Akpabio, ya ba da umarnin a gudanar da zaman taron gaggawa.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, “An bukaci Sanatoci da su yi dukkan shirye-shiryen halartar taron domin za a tattauna batutuwan da suka shafi kasa baki daya.
“Mun yi nadamar duk rashin jin dadin da wannan katsewar hutun zai haifar. Na gode da yadda kuka saba.”
Ku tuna cewa wasu ‘yan Najeriya sun shirya gudanar da zanga-zanga a fadin kasar a ranar 1 ga watan Agusta saboda tsananin matsin tattalin arziki da yunwa a kasar.