Majalisar Dattawan Najeriya ta amince da kafa kwamitin wucin gadi domin shirya taron ƙasa na kwana biyu kan matsalolin tsaro a birnin Abuja.
Taron na da nufin magance matsalolin tsaro da ke addabar ƙasar ta hanyar haɗa kai da duk hukumomin gwamnatin tarayya da jihohi da kananan hukumomi – tare da sarakunan gargajiya da kuma sauran masu ruwa da tsaki a fannin tsaro.
Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya amince da kudirin kuma ya umurci kwamatin wucin gadin da ya fara shirye-shiryen taron nan take.
“Dole ne a tsara taron ta yadda zai samar da matakan aiwatarwa, ba wai kawai yin taro na nuna bajinta ba,” in ji shi.
Ana sa ran taron zai samar da mafita mai amfani da haɗin kai ga matsalolin da ke barazana ga zaman lafiyar kasa.
A zaman majalisa da aka gudanar a ranar Talata, ‘yan majalisa sun tattauna tasirin sake shirya irin wannan taro, inda suka nuna cewa tarukan baya ba su haifar da gamsasshen sakamako ba.