Majalisar Wakilai ta kasa ta ƙaddamar da bincike kan ƙorafin da ‘yan ƙasa ke yi kan yawan cazar kuɗi da bankunan kasuwanci ke yi.
Yayin zamanta na jiya Laraba, majalisar ta umarci kwamatinta mai kula da harkokin bankuna da kuɗi da ya gudanar da bincike sannan ya kawo rahotonsa cikin mako huɗu masu zuwa.
Matakin ya biyo bayan ƙorafe-ƙorafen da mutane ke yi ne game da kuɗaɗe daban-daban da bankuna ke cire musu a matsayin ladan aikinsu da kuma na gudanarwa.
Kuɗaɗen sun haɗa da na tura kuɗi tsakanin bankuna da cire kuɗi daga na’urar ATM da ladan tura wa mutum saƙon tes da kuɗin gudanarwar katin ATM ɗin da kuma na sayen kayayyaki ta intanet.