Kakakin Majalisar Wakilai Tajudeen Abbas ya ce, majalisar ta 10 za ta yi kokarin karfafa rundunar sojojin Najeriya da sauran hukumomin tsaro domin tunkarar kalubalen tsaro a kasar.
Abbas, wanda ya bayyana hakan a wani taron kwanaki biyu bayan rantsar da mambobin kwamitin tsaro na majalisar, ya yi kira da a hada karfi da karfe domin tunkarar kalubalen tsaro masu sarkakiya a kasar.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Mista Musa Krishi, babban mai baiwa shugaban shawara kan harkokin yada labarai da wayar da kan jama’a shawara, ya fitar a Abuja ranar Asabar.
Ya bayar da shawarar samar da cikakken tsarin tsaro na kasa, inda ya kara da cewa akwai bukatar a kara karfin rundunar soji da sauran hukumomin tsaro.
Abbas ya ce majalisar wakilai ta 10 za ta ci gaba da tallafawa kokarin hukumomin tsaro ta hanyar isassun kudade, samar da kayan aiki na zamani, horaswa da inganta jin dadin jami’an tsaro.