fidelitybank

Majalisa za ta binciki yadda wutar Najeriya ke lalacewa

Date:

Majalisar Wakilai ta umarci kwamitinta da ke kula da harkokin wutar lantarki ya gudanar da bincike kan matsalar yawan lalacewar layin samar da lantarki na ƙasar, ya kuma bayar da rahoto cikin mako uku.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, matakin ya biyo bayan amincewa da buƙatar da ɗan majalisar Mansur Mano Soro, daga jihar Bauchi ya gabatar a zamanta na yau Laraba.

Ɗan majalisar ya bayyana damuwa kan matsalar lalacewar layin lantarkin na ƙasa da ta ƙi ci ta ƙi cinyewa a kwanakin nan, lamarin da ke jefa ƙasar cikin rashin wuta tare da jefa ‘yan ƙasar cikin matsin rayuwa da suke fama da shi.

Ya ce, wutar lantarki aba ce da ta zama wajibi wajen bunƙasar tattalin arziƙi da kuma cigaban duk wata ƙasa.

Hon. Mansur ya nuna takaicinsa yadda aka samu matsalar lalacewar layin wutar na ƙasa sau takwas a cikin wannan shekara ta 2024 kaɗai, inda ya bayyana hakan a matsayin abin damuwa da takaici.

Ɗan majalisar ya ce sakamakon matsalar lalacewar, gaba ɗaya yankin arewa maso yamma da kuma arewa maso gabas na ƙasar sun kasance cikin duhu, da uwa uba ƙarin tsanani na tsadar rayuwa.

Ya ƙara da cewa abin takaici ne yadda matsalar ke faruwa a daidai lokacin da ministan wutar lantarkin ke ba wa ‘yan Najeriya tabbacin ingancin samar da wutar, abin da ya sa har gwamnati ta ce ya sa dole ta ƙara kuɗin wutar ga masu amfani da ita na rukunin farko ko babban layi (Band A ).

bbc news nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp