fidelitybank

Majalisa za ta binciki yadda jiragen shugaban kasa ke lalacewa

Date:

Kwamitin tsaron ƙasa da bayanan sirri na majalisar wakilan Najeriya ya yanke shawarar kafa kwamitin ƙawararru don maganace matsalar da ke janyo yawan lalacewar jiragen sama na fadar shugaban kasar.

A jiya Litinin ne ƴan kwamitin suka yi wata ganawar sirri da kwamandan da ke kula da jiragen saman shugaban ƙasar, Air Vice Marshal Olayinka Olusola, a majalisar, a Abuja, domin tattaunawa a kan abin da ya kai ga Shugaba Bola Tinubu da mataimakinsa Kashim Shettima suka yi amfani da jiragen haya a kwanan nan.

A watan Afirilu ne Shugaban ya yi amfani da jirgin haya daga Netherlands zuwa Saudiyya domin halartar taron koli na duniya kan tattalin arziƙ.

Haka kuma mako biyu da ya gabata aka soke tafiyar da Mataimakin Shugaban Ƙasar Kashim Shettima zai yi inda zai wakilci Shugaba Tinubu a taron koli na hadin gwiwa tsakanin Amurka da Afirka kan kasuwanci saboda matsalar da jirgin da zai hau ya gamu da ita.

Shugaban kwamitin tsaro na majalisar Ahmad Satomi ya ce a muhawarar da suka yi kan batun, ƴan majalisar sun yanke shawarar gayyatar mai bai wa shugaban kasar shawara kan tsaro Nuhu Ribadu da kuma kwamandan da ke kula da jiragen fadar shugaban kasar da su je su yi bayani kan yawan lalacewar jiragen saman duk da maƙudan kuɗaɗen da ake ware musu a kasafin kuɗin duk shekara don kula da su.

vanguard newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp