fidelitybank

Majalisa za ta binciki shirin samar da kayayyakin noma na Tinubu

Date:

Majalisar wakilai ta umurci kwamitinta na harkokin samar da kayayyakin noma da ayyuka da ya gudanar da bincike kan rashin kawo injinan noma guda 2,000, kayan aiki, da taraktocin girbi guda 100 cikin wa’adin da aka tsara a wata yarjejeniya ƙarƙashin Shirin Tsaron Abinci na Shugaban Ƙasa da Shirin Inganta Noman zamani na Renew Hope.

Haka kuma, kwamitin zai binciki matsayin masana’antar haɗa injinan noma da aka yi yarjejeniya a kai.

An kuma umarci kwamitin da ya binciki yadda aka samar da kuma rarraba kayan aikin gona ƙarƙashin Ma’aikatar Harkokin Noma ta Tarayya tare da miƙa rahoto cikin makonni hudu don ɗaukar mataki.

Wannan umarni ya biyo bayan amincewa da kudurin da Hon. Saba Ahmed Adam ya gabatar a zauren Majalisa a ranar Talata.

A yayin gabatar da kudurin, ya bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ayyana dokar ta-baci kan samar da abinci a ranar Alhamis, 13 ga Yuli, 2023. Shirin da aka tsara don samar da abinci da samar da injinan noma na zamani a faɗin ƙasar.

Muhimman yarjejeniyoyi da aka shiga:

Sune Samar da taraktoci 2,000 da kuma injinan girbi guda 100 kowace shekara.

Gina masana’antar haɗa taraktoci a Najeriya, wanda zai ci Dala miliyan 70,041,733.80 da ₦2,981,739,134.30.

Sai Yarjejeniya ta tsawon shekaru 5 don gina masana’anta da za ta samar da taraktocin guda 2,000 da kayan aikin noma 9,022 kowace shekara.

Sai dai Hon. Adam ya bayyana damuwa cewa shekara guda bayan sanya hannu kan yarjejeniyoyin da Asusun Ci Gaban Noma na Ƙasa da Ma’aikatar Noma ta Tarayya, babu ko da tarakta ɗaya da aka kawo, duk da yawan kuɗaɗen da aka kashe.

Majalisar tace za a gudanar da binciken domin tabbatar da gaskiya da kula da yadda ake kashe dukiyar jama’a.

legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp