fidelitybank

Majalisa za ta binciki shirin samar da kayayyakin noma na Tinubu

Date:

Majalisar wakilai ta umurci kwamitinta na harkokin samar da kayayyakin noma da ayyuka da ya gudanar da bincike kan rashin kawo injinan noma guda 2,000, kayan aiki, da taraktocin girbi guda 100 cikin wa’adin da aka tsara a wata yarjejeniya ƙarƙashin Shirin Tsaron Abinci na Shugaban Ƙasa da Shirin Inganta Noman zamani na Renew Hope.

Haka kuma, kwamitin zai binciki matsayin masana’antar haɗa injinan noma da aka yi yarjejeniya a kai.

An kuma umarci kwamitin da ya binciki yadda aka samar da kuma rarraba kayan aikin gona ƙarƙashin Ma’aikatar Harkokin Noma ta Tarayya tare da miƙa rahoto cikin makonni hudu don ɗaukar mataki.

Wannan umarni ya biyo bayan amincewa da kudurin da Hon. Saba Ahmed Adam ya gabatar a zauren Majalisa a ranar Talata.

A yayin gabatar da kudurin, ya bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ayyana dokar ta-baci kan samar da abinci a ranar Alhamis, 13 ga Yuli, 2023. Shirin da aka tsara don samar da abinci da samar da injinan noma na zamani a faɗin ƙasar.

Muhimman yarjejeniyoyi da aka shiga:

Sune Samar da taraktoci 2,000 da kuma injinan girbi guda 100 kowace shekara.

Gina masana’antar haɗa taraktoci a Najeriya, wanda zai ci Dala miliyan 70,041,733.80 da ₦2,981,739,134.30.

Sai Yarjejeniya ta tsawon shekaru 5 don gina masana’anta da za ta samar da taraktocin guda 2,000 da kayan aikin noma 9,022 kowace shekara.

Sai dai Hon. Adam ya bayyana damuwa cewa shekara guda bayan sanya hannu kan yarjejeniyoyin da Asusun Ci Gaban Noma na Ƙasa da Ma’aikatar Noma ta Tarayya, babu ko da tarakta ɗaya da aka kawo, duk da yawan kuɗaɗen da aka kashe.

Majalisar tace za a gudanar da binciken domin tabbatar da gaskiya da kula da yadda ake kashe dukiyar jama’a.

daily post nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp