fidelitybank

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Date:

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka mai neman tabbatar da tsarin karɓa-karɓan shugabanci a Najeriya.

Wannan na daga cikin aikin da majalisar ke yi na gyaran wasu sassa shida na kundin mulkin ƙasar, waɗanda a baya suka gaza tsallake karatu na biyu a zauren majalisar.

Zaman majalisar na ranar Talata wanda shugabanta Abbas Tajudeen ya jagoranta ya yi muhawara a kan ƙudirin sannan ya cimma matsayar yin watsi dashi kamar yadda ya yi wa sauran ƙudirorin da aka gabatar da su tare.

Sai dai ana sa ran batun zai ƙara tasowa a zaman majalisar wakilan na yau Laraba domin sake tafka muhawa da ɗaukar matsaya a kai.

Wasu daga cikin ƴan majalisar da suka yi muhawara a kan ƙudirin sun ce a yanzu haka jam’iyyun siyasar Najeriya suna da irin nasu tanadi na tantance karɓa-karɓan shugabanci a Najeriya, kuma akwai hukumar tabbatar da daidaito, wadda ke aikin da ake neman ƙudirin ya yi.

nigerianewspapers.com.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...
X whatsapp